• Home
  • Contact Us
  • About us
  • Privacy Policy
Saturday, September 12, 2026
New Citizen
  • Login
  • Home
  • Nation
  • Politics
  • Business & Economy
  • Health
  • Education
  • Sport
  • Arts & Life
  • Culture & Entertainment
  • World
  • Perspectives
  • About us
  • Home
  • Nation
  • Politics
  • Business & Economy
  • Health
  • Education
  • Sport
  • Arts & Life
  • Culture & Entertainment
  • World
  • Perspectives
  • About us
No Result
View All Result
New Citizen
No Result
View All Result
Home Nation

by Admin-content
May 8, 2026
in Nation
0
0
SHARES
5
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

An kama Bello Boɗejo, ɗan takarar kujerar Sanata na APC a Taraba

 

READ ALSO

Uba Sani appoints 3 commissioners, aides, others

NOUN appoints Ramatu Ibrahim acting Bursar after Marafa’s death

Jami’an tsaro sun kama Bello Boɗejo, ɗan takarar neman kujerar Sanata mai wakiltar Taraba ta Tsakiya a ƙarƙashin jam’iyyar APC, a daren Alhamis a Jalingo, babban birnin Jihar Taraba.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa Boɗejo, wanda shi ne shugaban ƙungiyar makiyaya ta Miyetti Allah Kautal Hore, ya isa Jalingo tun da farko a cikin jirgin sama mai zaman kan sa ta filin jirgin sama na Ɗanbaba Suntai da misalin ƙarfe 1:20 na rana.

Dubban magoya bayan sa daga ƙananan hukumomi biyar da suka haɗa yankin sanatocin Taraba ta Tsakiya ne suka tarbe shi.

Da yake magana da Daily Trust ta wayar tarho, mataimakin sa na musamman, Umar, ya ce an kama ɗan takarar APC ɗin ne bayan ya kai ziyara wasu ofisoshin hukumomin tsaro tare da wasu na kusa da shi a siyasa.

A cewar sa, an kama shi ne a ɗaya daga cikin ofisoshin tsaron jim kaɗan bayan ya yi jawabi ga magoya bayan sa a sakatariyar APC ta jihar da ke Jalingo.

Umar ya ce an umurci mutanen da suka raka shi da su fice nan take, yayin da aka tsare Boɗejo.

“A halin yanzu, ba mu san inda aka kai shi ba,” inji shi.

“Jami’an tsaron da suka raka shi tare da ba shi kariya daga Abuja zuwa Jalingo su ne daga baya suka kama shi.

“Har yanzu ba a sanar da mu dalilin kama shi ba, kuma babbar damuwar mu yanzu ita c e ba mu san inda ake tsare da shi ba,” inji Umar.

Kafin a kama shi, Boɗejo ya shaida wa ’yan jarida a sakatariyar APC cewa ya sayi fom ɗin tsayawa takarar sanata kuma ba zai janye wa kowane ɗan takara ba.

Ya jaddada cewa yana nan daram a takarar kuma ba zai miƙa wuya ga matsin lambar da ake masa na janye takarar sa ba.

“Na shiga wannan takara ne domin in yi nasara, kuma babu wanda zai tilasta mini na janye,” inji shi.

Har ila yau, ɗan takarar APC ɗin ya bayyana cewa kwamitin maslaha da ake cewa Gwamna Agbu Kefas ya kafa domin tattaunawa da ’yan takara a yankunan sanatoci uku na jihar bai tuntube shi ba.

“Kwamitin maslahar da gwamnan ya kafa bai tuntuɓe ni ba, kuma ina so in bayyana a sarari cewa ba zan janye wa kowa ba, ko da kuwa akwai matsin lamba,” inji Boɗejo.

Wannan ba shi ne karo na farko da aka kama shi ba.

A 2024, jami’an Hukumar Tsaro ta DSS sun kama shi bisa zargin kafa ƙungiyar sintiri a Jihar Nasarawa.

An kama Boɗejo a hedikwatar Miyetti Allah Kautal Hore da ke Kasuwar Shanu ta Tudun Maliya, Kilomita 22, kan hanyar Abuja-Keffi Expressway, Tudun-Wada, Ƙaramar Hukumar Karu ta Jihar Nasarawa.

An ce jami’an DSS tare da wasu sojojin rundunar sojin Nijeriya sun mamaye hedikwatar Miyetti Allah da misalin ƙarfe 3:40 na yamma, sannan suka tafi da shi bayan sun kama shi a ƙofar shiga.

Har yanzu ba a san ko wannan sabon kamen yana da alaƙa da siyasa ko kuma batun tsaro ba.

Previous Post

Academy of Management hails Mande’s appointment as Director NOUN Business School

Next Post

Police arrest 8 suspected kidnappers, recover arms in Nasarawa

Related Posts

Governor Uba Sani set to distribute medical equipment to primary health care facilities in Kaduna today
Nation

Uba Sani appoints 3 commissioners, aides, others

September 10, 2026
NOUN appoints Ramatu Ibrahim acting Bursar after Marafa’s death
Education

NOUN appoints Ramatu Ibrahim acting Bursar after Marafa’s death

September 8, 2026
Tinubu mourns Emir of Gumel, hails his 46-year reign
Nation

Tinubu mourns Emir of Gumel, hails his 46-year reign

September 3, 2026
Kaduna inaugurates Media, Education, Livestock boards to drive reforms
Nation

Kaduna inaugurates Media, Education, Livestock boards to drive reforms

September 3, 2026
Next Post
Police arrest 8 suspected kidnappers, recover arms in Nasarawa

Police arrest 8 suspected kidnappers, recover arms in Nasarawa

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recent Posts

  • Uba Sani appoints 3 commissioners, aides, others
  • 2027: Idris urges Niger APC leaders to back Tinubu’s reforms, consolidate against
  • Umaisha gets Special Recognition Award at Fortham Exhibition
  • NOUN appoints Ramatu Ibrahim acting Bursar after Marafa’s death
  • CBN strengthens supervisory focus on terrorism financing risk

Recent Comments

No comments to show.

Recent Posts

  • Uba Sani appoints 3 commissioners, aides, others
  • 2027: Idris urges Niger APC leaders to back Tinubu’s reforms, consolidate against
  • Umaisha gets Special Recognition Award at Fortham Exhibition
  • NOUN appoints Ramatu Ibrahim acting Bursar after Marafa’s death

Quick Links

  • Home
  • Contact Us
  • About us
  • Privacy Policy
No Result
View All Result
  • Home
  • Nation
  • Politics
  • Business & Economy
  • Health
  • Education
  • Sport
  • Arts & Life
  • Culture & Entertainment
  • World
  • Perspectives
  • About us

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!